Gambiya ta ce kamfanin maganin tarin Indiya na da laifin kan mutuwar yara a ƙasar



Maganin tari na Maiden pharma

Asalin hoton, WHO

Bayanan hoto,

Hukumar lafiya ta duniya ta gshawarci mahukunta da su dai na siyar d maganin tarin guda hudu da aka samar da su a India

Wani kwamitin majalisar dokokin Gambiya ya bukaci a hukunta kamfanin samar da maganin tari na kasar Indiya da ake zargin ya yi sanadiyar mutuwar kusan yara 70 a kasar.

Kwamitin ya ce laifin kamfanin Maiden Pharmaceticals ne da ya shigo da maganain da yake gurbatace, zuwa kasar don haka dole ya amince da aikata ba daidai ba.

Hukumar lafiya ta duniya ta yi gargaadi a watan Octoban da ya gabata, inda ta shawarci mahukunta da su dakatar da sayar da maganin tarin.
Sai dai kamfanin Maiden Pharmaceutical ya musanta zargin.

Dakin gwaje-gwaje kimiyya na gwamnatin India, da ya gudanar da binciken maganin tarin, ya gano cewa suna an “suna bin ƙa’idar da aka gindaya wajen samar da maganin”.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like