Ganawar da ‘yan majalisar wakilan jam’iyyun adawa suka yi a Najeriya sun yi azarbabi – Masana



Majalisar wakilan Najeriya

Asalin hoton, OTHER

Masu sharhi kan harkokin siyasa a Najeriya na ci gaba da tsokaci a kan ganawar da ‘yan majalisar wakilan da suka fito daga bangaren jam’iyyun hamayya suka yi a makon nan.

Ganawar dai ta samu halartar sabbin ‘yan majalisun da kuma wadanda aka sake zaba domin wakiltar jama’arsu a majalisa ta 10 da ake shirin kafawa a watan Yunin 2023.

Farfesa Kamilu Sani Fagge, malami ne a tsangayar siyasa a Jami’ar Bayero ta Kano, ya shaida wa BBC cewa, irin wannan ganawa rikita-rikitar siya ce kawai.

Ya ce: “ A gaskiya sun yi sauri wajen gudanar da wannan taro, to amma ina ga sun yi kokari ne da ake cewa a tauna tsakuwa don aya ta ji tsoro domin idan an zo an rantsar da majalisar, kuma ba su yi wani abu da zai kawo rudani ba, to ko shakka babu ba za a yi da su a majalisar ba.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like