Ganawar Ministan Harkokin Wajen Iran Da Takwaransa Na Kasar Cote De Voire


4bka20504e96d2fti4_800c450

 

 

Muhammad Jawad Zarif Ya gana da takwaransa na Cote De Voire Abdullah Mabry, a nan Tehran a yau lahadi

Muhammad Jawad Zarif Ya gana da takwaransa na Cote De Voire Abdullah Mabry, a nan Tehran a yau lahadi.

Majiyar diplomasiyya anan Tehran ta sanar da cewa; Ministocin biyu sun yi ganawar ne a nan Tehran, inda su ka tattauna hanyoyin bunkasa alaka a tsakanin kasashen su.

Ministan harkokin wajen kasar ta Cote De Voire Abdullah Mabry, ya yi ishara da taron kwamitin hadin guiwa na kasashen biyu wanda aka yi a shekarar 2017 a birnin Abidjan, sannan ya jinjinawa jamhuriyar musulunci ta Iran akan rawar da ta ke takawa ta fuskar siyasa da tattalin arziki.

Bugu da kari, Mabry ya kara da cewa; Kasashen biyu kuma za su iya aiki tare a fagagen ilimi da bankuna da aikin gona da kare hakkin bil’adama da fada da ta’addanci da muggan kwayoyi.

You may also like