Sanata Rabiu Musa Kwankwaso dake wakiltar mazabar Kano t Tsakiya ya tallafawa matasa 3007 da suka fito daga mazabarsa.
An zabo wadanda suka ci gajiyar shirin daga kananan hukumomi 15 dake mazabar.
A jawabinsa na bude taro shugaban kungiyar Kwankwasiya, Barrister Aminu Dala ya shawarci wadanda suka ci gajiyar shirin da su tabbatar sun karbi katin zaben su domin su kafa gwamnati a shekarar 2019.
Ana sa jawabin shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar, Danburan Abubakar Nuhu, ya ce matasa sune kashin bayan kowanne irin cigaba saboda haka akwai bukatar a taimaka musu su zamo masu dogaro da kai.
Nuhu ya tabbatar da cewa idan kwankwasiya ta kafa gwamnati to za a samar da wasu karin shirye-shirye na tallafawa mutane domin rage zaman banza a tsakanin matasa.
Darakta Janar na Gidauniyar Kwankwasiya, Alhaji Sanusi Surajo Kwankwaso ya yabawa sanatan kan gudunmwar inda ya ce kudin da aka bayar na tallafin zai taimakawa wadanda aka bawa.