Gobara ta kashe mutum goma a Faransa



.

Asalin hoton, Olivier Klein

Mutum goma ne suka mutu, ciki har da kananan yara biyar, sakamakon wata gobara da ta tashi a wani gida a kusa da Lyon da ke Faransa, a cewar hukumomin karamar hukumar.


Wata sanarwa da hukumomi suka fitar ta ce wata “gobara mai dan girma” ta tashi a ginin mai hawa bakwai da ke unguwar Vaulx-en-Velin.

Mutum hudu na cikin mawuyacin hali yayin mutum goma suka ji kananan raunuka, cikinsu har da ma’aikatan kashe gobara guda biyu.

Ma’aikatan kashe gobara 170 ne suka yi ta fama har ta kai su ga kashe ta.

Olivier Klein, ministan birane da gidaje na lardin Borne, ya wallafa sako a shafinsa na Tuwita ranar Juma’a da safe inda ya ce: “Alkaluman mutanen da suka mutum sun jefa mu cikin tashin hankali.”



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like