Godwin Emefiele: Abin da ya kamata ku sani game da batun kama gwamnan CBN



Gwamnan CBN Godwin Emefiele

Asalin hoton, GODWIN EMEFIELE/TWITTER

Rahotannin da ke kara-kaina a wasu kafafen yada labarai na cewa hukumar tsaron farin kaya na shirin kama gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele.

Wata babbar kotu a Abuja babban birnin kasar ta yi watsi da bukatar DSS ta kamawa da tsare Mista Emefiele.

DSS na tuhumar Godwin da laifukan da suka shafi taimakawa ta’addanci, sai dai kotun ta ce hukumar ta koma ta samo ƙwararan hujjoji da shaidu kafin ta sake dawowa gabanta kan batun.

Abin da kotu ta ce game da batun Emefiele

Wani mai suna US Gambarawa shi ne ya shigar da karar a madadin hukumar tsaron farin kaya ta DSS a ranar 7 ga watan Disambar 2022.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like