Gwamnatin Buhari ta dora laifin tabarbarewar Tattalin Arziki kan gwamnatin Jonathan


 

Ministar kudi ta Najeriya Misis Kemi Adeosun ta bayyana cewa, ba manufofin gwamnatin Buhari ba ne suka janyo matsalar tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar ba, inda ta ce, gwamnatin baya ce ke da alhakin halin da aka fada.

Ministar ta zanta da ‘yan jaridu bayan taron majalisar zartarwa da aka gudanar a ranar Larabar nan a fadar shugaban kasa, inda ta ce, matsalar tattalin arziki ba abu ne da ya afku a rana daya ba.

Ta ce, wannan matsala ta faro ne shekaru 6 da suka gabata inda aa dinga kashe kudade a Najeriya kan bukatun yau da kullum maimakon a gudanar da manyan aiyuka na cigaban kasa.

A yanzu kuma gwamnati mai ci na ta kokarin ganin ta warwa wannan matsala.

A yanzu dai Najeriya na fuskantar matsalar tattalin arziki.

You may also like