Gwamnatin Katsina za ta ɗauki likitoci 54 aiki da kuma ma’aikatan jinya 600 


Gwamnatin jihar Katsina za ta ɗauki ƙarin sababbin likitoci 54 aiki, ma’aikatan jiya 600 da kuma sauran ma’aikatan kula da lafiya a asibitocin jihar.

 Gwamna Aminu Bello Masari wanda ya bayyana haka a ƙarshen mako ya lura cewa yinkurin daukar ma’aikatan zai inganta harkar kula da lafiya a jihar.

A cewarsa zuba jarin da gwamnatinsa take a fannin lafiya ya na haifar da ɗa mai ido domin tafiye-tafiye zuwa wasu jihohin ganin likita ya ragu sosai.

Gwamnan ya ƙara da cewa sababbin na’urorin da gwamnatinsa ta   saka a Asibitin ƙwararru na Amadi Rimi sun ƙara inganta fannin kula da lafiya a jihar.

You may also like