Gwamnatin Neja Ta Nuna Fushinta Ga Kamfanin Wutar Lantarki


Gwamnatin jihar Neja ta nuna fushinta ga kamfanin bada wutar lantarki na AEDC kan yadda ake karancin wutar lantarki a duk fadin jiha duk da cewa manyan tashoshin samar da wutar lantarki na aje ba, Kainji da Shiroro duk a cikin jihar suke.

Mataimakin Gwamnan jihar, Alhaji Ahmed Ketso ya ce abisa kasancewar wadannan manyan tashoshin wutar lantarkin, ya kamata ne a rika samun wutar lantarki na awowi ashirin da hudu a jihar inda ya nemi kamfanin AEDC ya gaggauta kawo karshen wannan matsalar.

A bangarensa, Shugaban kamfanin AEDC, Injiniya Earnest Mupwaya ya koka ne kan yadda masu Hulda da kamfanin ba su son biyan kudin wuta inda ya ce a halin yanzu kamfanin na bin bashin Naira Bilyan 40. Ya ce kamfanin zai rika samar da wadataccen wutar lantarki da zarar mutane suka fara biyan kudin wuta akai akai.

You may also like