Gwamnoni Sun Gana Da Kamfanin China Akan Batun Farfado Da Harkar Noma



Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje da takwarorinsa na jihohin, Jigawa, Osun, Ebonyi, Delta, Kebbi, Zamfara, Katsina, Sokoto da Kaduna sun gana da wani kamfanin noma na kasar China a ‘CAMALO’ a ofishin ministan noma Cif Audu Ogbeh. 
Majiyarmu ta gano cewa an yi zaman ne tsakanin bangarorin biyu don kulla hadin guiwa domin samar da hatsi da rogo da alkama a jihohin.
Shirin dai zai taimaka wajen cimma muradin Gwamnatin tarayya na rage dogaro da man fetur wajen samun kudaden shiga zuwa komawa fannin noma da kiwo.

You may also like