Gwamnonin Arewa Sun Tsayar Da Buhari A Matsayin Dan Takararsu A 2019



A yau Juma’a ne, Gwamnonin jihohin Kaduna, Malam El Rufa’i, Kano, Umar Ganduje, Niger, Abubakar Sani, Adamawa, Jubrilla Bindow, Kogi, Yahaya Bello, Yobe, Ibrahim Geidam suka tsayar da Shugaba Muhammad Buhari a matsayin dan takarar Shugaban kasa a 2019.

Gwamnonin sun cimma wannan matsayin ne bayan sun halarci Sallar Juma’a da Buhari a fadarsa inda Gwamnan Kaduna, Malam El Rufa’i ya jaddada cewa Buhari dan Nijeriya ne kuma yana da ‘yancin sake tsayawa takara idan har yana sha’awar yin hakan.

You may also like