Hajjin 2023: Saudiyya ta ware wa Najeriya kujeru 95,000



.

Asalin hoton, NAHCON

Saudiya ta dawo wa da Najeriya adadin kujerun da ta saba ba ta sama da 95, 000, na mutanen da za su je aikin Hajji a 2023.

Hukumar ƙasar ta Saudiya ta bayyana hakan ne a wata ganawa da hukumar alhazan Najeriya, a yau Laraba.

Suwaiba Ahmad, mai magana da yawun hukumar alhazan Najeriya ce ta tabbatar wa BBC matakin na Saudiya.

“Saudiya ta dawo da Najeriya kujerun da ta saba ba ta 95, 000, wanda a baya ta rage suka koma, 45, 000 saboda matsalar cutar korona, wanda shi din ma ba mu iya cikewa ba, saboda an bayar da shi a kurarren lokaci



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like