‘Hankalinmu ya tashi’ – iyalan Indiyawan da Najeriya ta kama da zargin satar mai



  • Marubuci, Imran Qureshi
  • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hindi
'Yan Indiya 16 na cikin matafiya a jirgin ruwa da Najeriya ta ƙwace jirginsu a watan Nuwamba
Bayanan hoto,

‘Yan Indiya 16 na cikin matafiya a jirgin ruwa da Najeriya ta ƙwace jirginsu a watan Nuwamba

Ba sabon abu ba ne matafiya su shafe tsawon lokaci ba tare da iyalansu ba a lokutan Kirsimeti da bukukuwa.

Amma wannan karon ya fi zafi ga iyalan Indiyawa 16 matafiya da Najeriya ke tsare da su tun daga watan Nuwamba, lokacin da hukumomi suka ƙwace jirgin ruwansu.

Mutanen, dukkansu maza, na cikin matafiya 26 da ke cikin jirgin mai suna MT Heroic Idun. Sauran ‘yan Sri Lanka ne da Philippines da kuma Poland.

Hukumomin Equatorial Guinea ne suka fara tare jirgin wanda mallakar kamfanin OSM Maritime Group ne na ƙasar Norway a watan Agusta bayan Najeriya ta tsegunta mata cewa akwai yiwuwar matafiyan sun saci ɗanyen mai daga ƙasar.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like