Harin bam ya kashe mutum tara ƴan gida ɗaya



...

Asalin hoton, Getty Images

Wasu hare-haren bam guda biyu da aka kai a tsakiyar lardin Hiraan na Somalia sun hallaka mutum tara na iyali guda.

Wani mataimakin shugaban ƴan sanda na yankin ya ce harin ya kuma kashe ƙarin mutum 26.

Ƙungiyar al-Shabab mai alaka da al-Qaeda ta ɗauki alhakin kai harin.

Kwamishinan yankin Mahas ya ce an yi niyyar kai harin ne a kan gidansa da kuma gidan wani ɗan majalisa.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like