Hukumar zabe ta Najeriya, INEC, ta dage shirin da take yi na tantance takardun neman kiranye da ta shirya za ta yi a kan dan majalisar dattawa Dino Melaye.
Hukumar ta fitar da wannan bayanin ne bayan da ta sami umarni daga wata kotu na ta dakatar da shirin nata.