Hukumar Kwallon Faransa ta hana a tsaya buda baki lokacin tamaula



Ramadan

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar kwallon kafar Faransa ta aike da sakon wasika ga rafli da cewar kada su tsayar da wasa domin masu azumi su buda baki a lokacin tamaula.

Ranar Juma’a aka ci gaba da wasannin Ligue 1, inda Marseille ta tashi 1-1 da Montpellier, bayan kammala wasannin kasa da kasa da Fifa kan ware ranakun.

Kamar yadda Mailonline ta wallafa, ta ce an samu sakon da hukumar ta aikewa alkalen tamaula a fadin kasar da cewar za ta dakatar da duk wanda ya tsayar da wasa domin shan ruwa ko buda baki a gefen fili lokacin da ake tamaula.

Musulmai na yin azumi a watan Ramadan tun daga farko har karshensa, inda aka bukaci kauracewa ci da sha tun daga asuba zuwa faduwar rana.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like