Hukumar kwallon Faransa ta nemi a hukunta Martinez



Martinez

Asalin hoton, OTHER

Hukumar kwallon kafar Faransa ta kai karar golan Argentina Emiliano Martinez, saboda salon murnar da ya yi a wasansu na karshe na gasar kofin duniya.

Martinez ya taka rawa sosai a wasan musamman a bugun fenareti da suka yi nasara.

To amma wasu hotuna sun nuna shi rike da diyar roba mai siffar dan wasan gaban Faransa, Kylian Mbappe, a lokacin da suke murnar lashe kofi a birnin Buenos Aires.

Wasu rahotanni sun ce har neman a yi shiru na minti daya ya yi ga Mbappe a dakin saka kaya bayan kammala wasan.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like