Imam Imam mai magana da yawun gwamnan jihar Sokoto ya rasu


Imam Imam mai magana da yawun gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal mutu.

Imam ya rasu da karfe uku na daren Juma’a a asibitin Nizamieye na yan kasar Turkiyya dake Abuja.

Abubakar Imam wani kaninsa shine ya tabbatar da mutuwarsa.

Za dai ayi jana’izarsa a masallacin Annur dake Abuja da misalin karfe 1:30 na rana bayan an kammala sallar Juma’a.

Yan uwa , abokanan aiki da kuma masu bibiyar kafafen yada labarai na cigaba da bayyana alhininsu na rasuwarsa a kafafen sadarwar zamani.

Marigayi dan asalin jihar Taraba ne ya rasu ya bar mata biyu da kuma ‘ya’ya hudu.

You may also like