Ina fuskantar matsin lamba don in bar Najeriya – Peter Obi



Peter Obi

Asalin hoton, Getty Images

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen Najeriya na 2023 Peter Obi ya mayar da martani kan wata murya da ke yawo a shafukan sada zumunta.

Ana zargin cewa muryar na wata tattaunawa ce ta waya tsakanin Obi da shugaban cocin Living Faith, Bishop Oyedepo.

Hakan na zuwa ne bayan kimanin kwana biyar da ɓullar muryar.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na tuwita a ranar Laraba, Obi ya ce ce-ce-ku-cen da ake yi kan muryar wata maƙarkashiya ce da jam’iyya mai mulkin Najeriya ke yi na tursasa masa ya bar Najeriya.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like