INEC za ta dakatar da yi wa mutane rijistar yin zaɓe kwanaki 60 kafin zaɓen 2019


Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Ƙasa INEC, ta ce cigaba da yiwa mutane rijistar kaɗa kuri’a da ake yi a ƙasa baki ɗaya za a dakatar da shi na wucin gadi kwanaki 60 kafin babban zaɓen ƙasa na shekarar 2019.

Hukumar cikin wata sanarwa da Solomon Soyebi, kwamishina a hukumar dake shugabantar kwamitin sadarwa da kuma ilimantar da masu kaɗa kuri’a ya fitar ranar Laraba a Abuja, ya ce za a dakatar da shirin ne saboda sauyi da aka samu a dokar zaɓe.

Soyebi ya bayyana cewa ya zuwa yanzu ƴan Najeriya sama da miliyan huɗu aka yiwa rijistar a ƙasa baki ɗaya ƙarƙashin shirin da aka fara ranar 27 ga watan Afirilun shekarar 2017.

” Shirin na cigaba da yin rijistar masu kaɗa kuri’a a duk ƙasa baki ɗaya zai bawa dukkanin ƴan Najeriya da suka cancanta,masu  shekara 18 zuwa sama waɗanda basu yi rijista ba a shirin da aka yi a baya damar yi a yanzu.

” Ya zuwa ya yanzu sama da mutane miliyan huɗu aka yiwa rijistar a duk faɗin ƙasar nan.

“Amma kamar yadda yake a sashi na 9 ƙaramin sashi na 5 na dokar zaɓen ƙasa ya bayyana cewa za’a dakatar da cigaba da yiwa mutane rijista kwanaki 60 gabanin babban zaɓen ƙasa wanda aka shirya gudanarwa cikin watan Faburairun 2019.

“Za a cigaba da shirin bayan an kammala zaɓen.”

You may also like