Iran ta yi tir da takunkumin Amirka | Labarai | DW



A lokacin da ya yi bayyani a shafinsa na Instagram, Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Nasser Kanani ya ce “Ya kamata Joe Biden ya yi tunani game da yadda kasarsa Amirka ta kare hakkin bil’adama kafin ya yi magana kan halin da ake ciki a Iran.”

Akalla mutane 92 ne aka kashe a Iran tun lokacin da aka fara zanga-zangar yin tir da mutuwar Mahsa Amini, a cewar kungiyar kare hakkin bil adama, yayin da hukumomi suka ce adadin wadanda suka mutu bai fi 60 ba ciki har da jami’an tsaro 12.

Dama dai jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Ali Khamenei, ya soki manufar Washington a jiya litinin, yana mai zargin Amirka da Isra’ila da ruruta wutar zanga-zanga da ta kasance mafi muni a Iran a cikin shekaru ukun da suka gabata.

 



You may also like