Isra’ila da Gaza: Yadda aka kwashe jarirai bakwaini daga asibitin Al-Shifa



UN personnel looking after one of the babies

Asalin hoton, WHO

Bayanan hoto,

Makomar jariran ya shiga garari a daidai lokacin da asibitin al-Shifa ke fuskantar ƙarancin man fetur da kuma dakatar da aiki

An kwashe jarirai bakwaini 31 daga asibitin al-Shifa da ke birnin Gaza, wanda Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta kwatanta da “sansanin mutuwa”.

An ɗauki jariran zuwa wani asibiti da ke kudancin birnin Rafah, kusa da iyaka da Masar.

Ɗaruruwan mutane, ciki har da marasa lafiya, suka bar al-Shifa a ranar Asabar.

Asibitin – wanda ya kasance mafi girma kuma na zamani a yankin – na karkashin ikon sojojin Isra’ila.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like