Ivory Coast ta ci wasa na biyu a neman shiga gasar kofin duniya



Ivory Coast

Asalin hoton, Getty Images

Ivory Coast ta ci Gambia 2-0, a wasa na bibiyu a rukuni na shida don neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da za a yi a 2024.

Daf da za su je hutu ne Ivory Coast ta ci kwallo ta hannun Christian Kouame, sannan ta kara na biyu saura minti hutu a tashi ta hannun Seko Fofana.

Da wannan sakamako, Ivory Coast wadda za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka a 2024, tana ta daya a rukuni na shida da maki shida.

Gabon ma maki shida ne da ita, wadda aka bai wa tazarar rarar kwallaye, bayan da Ivory Coasr ta durawa Seychelles 9-0 a wasan farko a cikin rukuni ranar Juma’a.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like