An Iza Keyar Wanda Ya Sanyawa Karensa Suna Buhari Zuwa Kurkuku


Joe-Fortomose-Chinakwe

Hukumar ‘yan sandan  jihar Ogun sun cigaba da tsare Joe Fortomose Chinakwe wanda ya sanyawa karensa suna Buhari a kurkuku.

Rundunar ‘yan sandan jihar ce dai ta gurfanar da Joe Fortomose Chinakwe a gaban kotun majistare a jiya Litinin, bisa zargin shirin tada zaune tsaye, sakamakon yawon da yake yi da karen sa, wanda ya rubuta sunan Buhari a sassan jikin karen.

Jim kadan, kotun dai ta bada belinsa, to sai dai bai cika sharudan beli ba, dan haka aka ci gaba da tsare shi a gidan kaso.

You may also like