Jami’an Tsaro Sun Rushe Husainiya Da Makaranta Mallakar ‘Yan Shi’a a Kaduna


 

Jami’an Tsaro cike da motoci 3 sun rushe sabuwar husainiyyah da ‘yan shia ke ginawa a garin Saminaka da ke jahar Kaduna a yau.

Haka kuma jami’an KASUPDA tare da rakiyar jami’an tsaro sun rusa muhallin makarantar mabiya shi’a wato Fudiyyah dake unguwar Babban dodo cikin garin Zariya.

‘Yan shi’an da dama dai na zargin gwamna El-Rufai da turowa a yi masu wannan rusau

Rahotanni sun nuna cewa bayan an rushe makarantar, jama’a sun yi ta kwasar kayayyakin dake cikinta suna awon gaba da su a matsayin ganima.

Ita kuma Husainiyyar dama an gina ta ne watanni biyu da suka gabata, don ci gaba da gudanar da tarurrukan mabiya Shi’a a Saminaka, kuma tun a lokacin wasu suka yi yunkurin tada rikici akan ginin, al’aamarin da ya sa gwamnatin Kaduna ta shigar da kara kotu, ita kuma kotu ta dakatar da ginin.

Rahotan ya kuma nuna cewa maganar har yanzu na kotu.

15056380_1091823394249423_9176834850797619290_n

15032912_1091871950911234_7196446198922685072_n

15109520_1091872147577881_7116225443774367938_nshiaa

 

cc: ALummata

You may also like