Jihohin da ake ƙarasa zaɓen gwamnoni da ‘yan majalisun dokoki a Najeriya



Nigeria supplementary polls

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa a Najeriya na ƙarasa zaɓuka kusan 100 da suka rage, ciki har da na gwamnoni a jihohin Kebbi da Adamawa.

An bayyana zaɓukan a matsayin waɗanda ba su kammala ba ne, lokacin babban zaɓe na ƙasa ranar 25 ga watan Fabrairu da kuma na ranar 18 ga watan Maris.

Baya ga zaɓen gwamnoni a jihohin Adamawa da Kebbi, za kuma a kammala zaɓukan ‘yan majalisar dattijai guda biyar da na ‘yan majalisar wakilai 31.

Akwai kuma zaɓukan ‘yan majalisun dokoki na jihohi guda 58 da ake ƙarasawa duk a yau Asabar.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like