An kai wa ‘yan sanda hari da wuka a Brussels


57f5d7cf8cb33

 

An kai wa wasu ‘yan sanda 2 hari da wuka a ciki da wuyansu a Brussels babban birnin kasar Beljiyom.

An samu nasarar kubutar da ‘yan sandan amma kuma sun samu raunuka kadan.

An harbi maharin da ya yi kokarin guduwa tare da kama shi.

A shekarar 1973 aka haifi maharin mai suna Hitcham kuma dan asalin kasar ta Beljiyom ne.

A gefe guda kuma jami’an tsaro sund auke wani kundhin leda da aka samu a tashar jirgin kasa ta birnin.

Binciken da aka yi ya nuna cewa, babu wani na fashewa a cikin ledar.

A watan maris din da ya gabata mutane 32 ne suka mutu sakamakon harin daaka kai a birnin Brussels.

Kasar dai na cikin fargabar barazanar ‘yan ta’adda.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like