Ka’idar cire kudin CBN ta raba kan majalisar dattawan Najeriya



Senate President

Asalin hoton, Senate Facebook

Kan ƴan majalisar dattawan Najeriya ya rabu biyu kan batun sabbin ƙa’idojin da babban bankin ƙsar CBN, ya fitar na ƙayyade cire kuɗaɗe.

Hakan ya faru ne a yayin gabatar da rahoton kwamitin da ke lura da sha’anin banki na majalisar dattijan kan sabbin tsare-tsaren da ka’idojin CBN din.

Wasu mambobin majalisar sun nuna goyon bayan tsarin na CBN yayin da wasu kuma suka nuna ƙin amincewa da sabbin ƙa’idoji cire kuɗaɗen.

Shugaban kwamitin Sanata Uba Sani ne ya gabatar da wannan rahoto a zaman da majalisar ta yi na ranar Laraba.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like