Kaikayi Ya Koma Kan MasheKiya A Isla’ila Inda Gobara Ta cinye Wani Yanki Na Kasar



Sun shirya mamaye filayen Musulmin Kudus Allah Ya aiko Gobara tana cinye Kasar. 

A yayin da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Israila game da shirin yin sabbin gine-gine a gabashin Kudus.


Kwamitin ya ce, akwai fargaba sosai game da yadda Israila ke shirin yin sabbin gine-gine a Kudus wanda ke da hadari wajen samar da zaman lafiya  a yankin.


Kawai ba zato ba tsammani sai Allah Ya aiko musu da gobarar daji ta fara cinye wani Yanki na kasar. Mutane sama da 10,000 sun kauracewa gidajen su.

You may also like