Kasafin Kudi: Buhari Ya Umarci Shugabannin Hukumomin Gwamnati Da Su Bayyana Gaban Majalisa


Shugaba Muhammad Buhari ya umarci shugabannin hukumomin gwamnati kan su gaggauta bayyana gaban majalisar tarayya don yin bayani game da bukatun da suka gabatar a cikin kasafin kudin bana.

Shugaban ya bayar da wannan umarnin ne a jiya bayan da shugabannin majalisar a karkashin jagorancin Sanata Bukola Saraki suka ziyarce shi a fadarsa inda suka koka kan yadda shugabannin hukumomin gwamnati ke kin bayar da hadin kai ga majalisar a kokarin da take yi na ganin ta kammala aikin kasafin kudin.

You may also like