Kin biyan kuɗin haya yasa wani mai gidan haya kona gidansa


Wani me gidan haya da aka bayyana da suna, Idemudia Obamonyi,ya kona gidan mahaifinsa da ya mutu ya bar masa bayan da mutanen dake haya a gidan suka gaza biyan kuɗin haya.

A cewar rahotanni shaguna sama 20 ne a gidan, dake layin Owobo bayan kasuwar Oba dake Benin babban birnin jihar Edo.

Mutane dake wurin ne suka jiyo Idemudia yana fadin cewa  a bari gidan ya kone tunda shi baya amfana da gidan.

 Wani mazaunin yankin mai suna,Ifaluyi Obasogie ya ce wannan abu ne da ba a saba jin irinsa ba ace mai gidan haya ya kona gidansa da kansa “Mun ga mutane suna riƙe shi yana cewa a bari gidan ya kone, bana samun ko kwabo daga shi.”

Wani dake haya a daya daga cikin shaguna dake a gidan,Justice Aigbekhan, ya ce sun biya kuɗin hayarsu amma Idemudia ya cigaba da tambayarsu kudi wai yana son yin bikin binne mahaifin nasa.

Tuni dai  jami’an tsaro suka damke shi.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like