Ko an samu ci gaba kan yaki da rashawa lokacin Buhari?



Shugaba Muhammadu Buhari

Asalin hoton, Getty Images

Yaƙi da cin hanci da rashawa na cikin muhimman abubuwan da Shugaban Najeriya mai barin-gado Muhammadu Buhari ya ce ya fi bai wa fifiko a tsawon shekara takwas na mulkinsa.

An yi ittifakin cewa matsalar ta cin hanci ita ce babban abin da ya yi wa ƙasar mafi yawan jama’a a Afrika tarnaƙi wajen samun cigaba ta kowace fuska.

Babu shakka idan akwai wata siffa da ta jawowa Shugaban Najeriyar farin jini a wajen talakawan ƙasar, ita ce gaskiyar da suka yi imanin yana da ita, kuma tunanin cewa shi ne kaɗai zai iya cire wa ƙasar dabaibayin da cin hanci da rashawa ya yi mata na tsawon gwamman shekaru.

Haka kuma yaki da matsalar ta cin hanci, na daga cikin manyan alkawuran yakin neman zaɓensa a duk tsawon shekaru 12 da ya kwashe yana neman shugabancin ƙasar.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like