Ko Messi zai ci Kofin Duniya ko Mbappe ne zai lashe na biyu a jere?



Messi Mbappe

Asalin hoton, Getty Images

Argentina za ta kara da Faransa a wasan karshe a Gasar Cin Kofin Duniya ranar Lahadi da Qatar ke karbar bakunci.

Ko Messi zai dauki Kofin Duniya na farko a tarihi, ko kuwa Mbappe zai lashe na biyu a jere a karawar da za su buga a filin wasa na Lusail.

Messi mai shekara 35, ya lashe Ballon d’Or bakwai da Copa America da sauran kofuna da yawa, amma bai taba daukar na Duniya ba.

Argentina mai Kofin Duniya biyu jumulla, amma rabon ta da shi tun 1986 karkashin jagorancin Diego Maradona.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like