Kotu Ta Bada Belin Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa Saminu Turaki 



Babbar kotun tarayya dake zamanta a Maitama,Abuja  ta bada belin tsohon gwamnan jihar jigawa Saminu Ibrahim Turaki. 

Hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC, ce ta kama tsohon gwamnan a Abuja lokacin da yake halartar bikin taron kaddamar da littafi.

Da yake bada belin, mai shari’a Yusif Halilu  ya umarci Turaki da ya mika takardunsa na tafiye-tafiye ga magatakardan kotun.

 Kotun ta kuma yi umarni da ya gabatar da mutane guda biyu da zasu tsaya masa, mazaunan Abuja da suke da aikin yi. 

A karshe mai shari’a Halilu ya umarci Turaki da yakai kansa Ofishin hukumar EFCC  a duk mako biyu  domin yasa hannu a rijista da za a bude masa  yau, har sai ranar da zai gurfana gaban kotun tarayya dake Jigawa, lokacin da kotun zata dawo hutun shekara a watan Satumba.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like