Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Yahaya Bello A Matsayin Gwamnan Kogi


 

images-12

 

 

Babbar kotu dake Abuja a yau Talata ta tabbatar da Yahaya Bello a matsayin zababben Gwamnan Jihar Kogi.

Kotun ta yi watsi da daukaka karar da Hon. James Faleke mataimakin Gwamnan da ya rasu Marigayi Abubakar Audu  ya shigar da kuma abokin takararsa a jam’iyyar adawa ta PDP Kyaftin Idris Wada.

Rahoton ya kara da cewa, kotun za ta bayyana hujjojinta a ranar 30 ga Satumba 2016.

You may also like