Kotu ta wanke tsohon gwamnan jihar Enugu daga zargin almundahana 


Wata kotun tarayya dake zamanta a Lagos ta kori dukkanin tuhume-tuhumen da akewa, Chimaroke Nnamani tsohon gwamnan jihar Enugu.

Hukumar Yaƙi Da Yiwa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati ta EFCC, ta tuhumi Nmandi da laifin naira biliyan ₦4.2 lokacin da yake riƙe da kujerar gwmnan jihar Enugu tsakanin shekarar 1999-2007.

An shirya gurfanar da shi gaban kotun a ranar Talata tun bayan da aka gurfanar da shi a shekarar 2007.

Ya yin zaman kotun na ranar, Ricky  Tarfa Lauyan Nnamani ya sanar da kotun sakamakon rokon da yayi na sasantawa da hukumar ta EFCC a wajen kotu a watan Yuli na shekarar 2015.

Duba da ɓukatar da lauyan ya shigar kotun ta amince da yarjejeniyar da suka cimma inda ta soke dukkanin tuhumar da ake wa tsohon gwamnan.


Like it? Share with your friends!

0

You may also like