Kotun Koli Ta Dakatar Da Wa’adin Daina Karbar Tsoffin Kudi




Kotun koli a Najeriya ta dakatar da gwamnatin tarayyar daga aiwatar da shirin daina karbar tsoffin kudi.

A ranar 10 ga watan nan na Fabrairu wa’adin da babban bankin kasar na CBN ya ayyana ya kamata ya fara aiki.

Sai dai yayin wani zama da ta yi a ranar Laraba, kotun kolin kasar mai alkalai bakwai, ta dakatar da shirin daina amfani da tsoffin kudaden har sai an kammala sauraren shari’ar.

A ranar Litinin jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara suka shigar da kara a kotun inda suka kalubalanci sabon wa’adin, wanda zai kare a ranar Juma’ar mai zuwa.

Tun da farko a ranar 31 ga watan Janairu babban bankin na CBN ya ce za a daina amfani da tsoffin takardun kudin naira 200, 500 da 1000.

Amma bayan korafe-korafe da aka yi ta yi, bankin ya kara kwanaki goma bayan sahalewar Shugaba Muhammadu Buhari.

Gabanin shigar da karar a kotu, gwamnonin jam’iyyar APC sun kai wa shugaba Buhari ziyara a fadarsa, inda suka nemi a kara wa’adin.

Ko da yake, ba su samu biyan bukata ba, amma shugaban na Najeriya ya ce za a shawo kan matsalar karancin kudaden cikin kwanaki bakwai.

A halin da ake ciki, kotun ta ba bankuna da sauran cibiyoyin hadahadar kudade a kasar umarni da su ci gaba da amfani da tsoffin kudaden har sai kotun ta yanke hukunci a zaman da za ta yi a ranar 15 ga watan Fabrairu.

Tun a watan Nuwambar bara, Najeriya ta soma fitar da sabbin kudaden da aka sauya wa fasali, sai dai karancin su ya jefa al’umar kasar cikin halin kakani-kayi.



Source link


Like it? Share with your friends!

2

You may also like