Ku Gaggauta Biyan Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Hakkunan Su –  NLC ga Gwamnatin Kano



Kungiyar gwadago ta kasa NLC ta yi kira ga gwamnatin jihar Kano ta hanzar kamala biyan albashin ma’aikata na watan Disambar daya gabata, da kuma na ‘yan fansho a jihar.
Shugaban kungiyar reshen Kano Kwamared Kabiru Ado Munjibir ne ya yi wannan kiran jim kadan bayan kamalla ziyara musamman a wasu kamfanoni biyar mallakin wani mutumin kasar China Mr Lee domin ganin ma’aikatan kamfanin sun sami yancin kafa kungiya.

You may also like