Ku San Malamanku tare da Gwani Sagir Usman Madabo



Bayanan bidiyo,

Ku latsa sama don kallon bidiyon

Ku San Malamanku tare da Gwani Sagir Usman Madabo

An haifi Gwani Sagir Usman Madabo a unguwar Madabo cikin birnin Kano, kuma ya fara karatunsa ne a hannun wani Mallam Kyauta. Ya sauke Al-Qur’ani ne da ƙarfin gwiwar Khalifa Isyaku Rabi’u.

Ya halarci Adakawa Firamare, wadda ya kammala a shekarar 1985, kafin ya tafi sakandiren Gwammaja 2 wadda ya kammala a 1990.

Gwani Sagir Madabo ya kuma halarci kwalejin nazarin shari’a da addinin Musulunci ta Aminu Kano wato Legal kafin ya wuce zuwa Jami’ar Bayero inda ya karanta babbar difloma a fannin nazarin harkokin shari’a.

A yanzu haka, karatun digirinsa na biyu a Jami’atun Nahda da ke Jamhuriyar Nijar, inda yake fatan kammalawa a 2023.



Source link


Like it? Share with your friends!

-1

You may also like