Ku san Malamanku tare da Malam Ibrahim Mai Ashafa



Bayanan bidiyo,

Ku San Malamanku da Malam Ibrahim Mai Ashafa

Fitaccen malamin nan na jihar Kano Malam Ibrahim Kabiru wanda aka fi sani da Malam Ibrahim Mai Ashafa ya ce ba bu inda ya fi burge shi cikin littafin Ashafa kamar babin suffofin Annabi Alaihissalam.

Malamain wanda aka haifa a jihar Kano a 1976, ya ce ya tashi ne a gaban Sheik Aliyu Harazimi, ya ce babu wani waje a cikin littafin Ashafa da ba ya da daɗin karantawa.

Kamar dai mafi yawan malamai, shi ma Malam ya fara karatunsa ne a gaban iyayensa kafin daga bisani a kai shi karatu gaban malamai.

“Mun fara da karatun Alƙurani mai girama hannun Malam Bala, daga baya muka koma hannun Malam Baffa gidan Sarkin Tsakuwa, kuma a nan ne muka yi haddar Alƙur’anin”.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like