Kungiyar Shi’a Sun Nuna Rashin Gamsuwa Bisa Nuna jagoran Su Ga Duniya Ba



Kungiyar Shi’a sun nuna rashin gamsuwa da matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na nunawa duniya Shugaban Kungiyar, Malam Ibrahim El Zakzaky bayan an rika yayata jita- jitar mutuwarsa a hannun jami’an tsaro.

Kakakin Kungiyar, Ibrahim Musa ya ce matakin gwamnatin ya saba hukuncin Babban kotun tarayya wadda ta nemi a saki El Zakzaky tare da biyansa diyya inda ya nuna cewa an yi kwaskwarima a faifan bidiyon da aka nuna El Zakzaky na bayani a takaice.

You may also like