Labarin matar da aka aura a matsayin ta biyar a Jamhuriyar Nijar



Hadizatou Mani
Bayanan hoto,

An sayar da Hadizatou Mani ga wani mutum karkashin koyarwar wahaya a Jamhuriyar Nijar

Daga Caroline Mwangi da Muktar Sadu Alize

An sayar da Hadizatou Mani-Karou ga wani basaraken kauye lokacin tana da shekaru 12, ta kuma zamo mace ta biyar a wurin mutumin a wani tsari da ake kira Wahaya ko ”mace ta biyar”, yanayi ne mai matukar tayar da hankali.

“Ba ni da wani ‘yanci; babu hutu, babu abinci, babu kwanciyar hankali,” in ji matar a shirin BBC na Mata 100, a lokacin tana gidansu da ke kudancin jamhuriyar Nijar.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like