Lalong ya gargadi Ortom kan dokar hana kiwon shanu



Gwamnan jihar Plateau Simon Lalong yace sai da ya shawarci takwaransa na jihar Benue, Samuel Ortom kan aiwatar da dokar hana kiwon shanu a fili.

Lalong ya fadi haka lokacin da yake tattaunawa da manema labarai dake  fadar shugaban kasa a yau bayan wata ganawa da yayi da shugaban kasa Muhammad Buhari.

A yan kwanakin nan an rawaito cewa fulani makiyaya sun kashe mutane da dama a jihar Benue.

A cewar Lalong ba fulani ne kaɗai ba, ke kiwon dabbobi.

Gwamnan yace jihar Filato na cin gajiyar zaman lafiyar da aka samu ne a jihar saboda gwamnati ta haɗa kai da kowa, fulani da manoma baki ɗaya.

Lalong ya kuma ce ya gamsu da shirin gwamnatin tarayya na samar da wurin kiwo a jihar a matsayin wata hanya ta kawo karshen rikicin dake faruwa tsakanin fulani makiyaya da manoma dake yawan faruwa.

You may also like