Ma’aikatan jinya na jihohi da kananan hukumomi da ke fadin kasar nana sun bi sahun takwarorinsu na cibiyoyin lafiya na tarayya wajen shiga yajin aiki.
Shugabannin ma’aikatan jinya na jihohin sun bayyana cewa sun yanke shawarar shiga yajin aikin ne saboda yajin aikin da ake yi a cibiyoyin lafiya na tarayya ya janyo marasa lafiya sun cika asibitocin da ke jihohi da kananan hukumomi.