Mai Mala Buni ya samu wa’adi na biyu a Yobe



Hukumar zaben Najeriya mai zaman kanta – INEC ta ayyana Mai Mala Buni na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar Yobe.

Da yake sanar da sakamakon zaben a Damaturu babban birnin jihar, babban jami’in da ke kula da zaben, Farfesa Umaru Pate ya ce Mai Mala Buni ya lashe zaben da kuri’u 317,113 a yayin da Sheriff Abdullahi na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 104,259.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like