Majalisar Amurka ta amince a tuhumi Trump da aikata manyan laifuka hudu



A Trump bust being held up during the day of the riot at the US Capitol

Asalin hoton, Getty Images

Wani kwamitin da ke binciken kutsen da aka yi wa ginin majalisar Amurka, Capitol a bara ya yanke shawara cewa a tuhumi tsohon Shugaba Donald Trump da aikata manyan laifuka, ciki har da na yunkurin hambare gwamnati.



Kwamitin da ‘yan jam’iyyar Democrat a majalisar ke jagoranta ya amince da gagarumin rinjaye domin ma’aikatar Shari’a ta kasar ta gurfanar da Mista Trump domin a yi masa shari’a.



Ranar 6 ga watan Janairun 2021 ne dai magoya bayan Mista Trump suka afka wa ginin majalisar, yayin da ake shirin tabbatar da JOe Biden a matsayin shugaban Amurka.



Mista Trump, wanda ya musanta aikata ba daidai ba, ya fitar da wata sanarwa da ke cewa kwamitin na jeka-na-yi-ka ne.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like