Makomar tallafin man fetur a Najeriya bayan Yunin 2023



..

Asalin hoton, Getty Images

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa zuwa Yunin 2023, za ta daina biyan kuɗin tallafin fetur da ta saba biya.

Ministar kuɗi da kasafi ta ƙasar Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a lokacin da ta ke gabatar da kasafin na 2023 ga jama’ar ƙasar.

Ta bayyana cewa a 2023, gwamnatin ta ware naira tiriliyan 3.36 ne kawai domin biyan tallafin fetur na wata shidan farko na shekarar.

Ta kuma ce wannan matakin na tafiya ne da ƙarin wa’adi na watanni 18 na cire tallafin da aka sanar a 2022.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like