Mamaki: Matashi Dan Shekaru 30 Ya Kashe Kansa Saboda Sun Sami Matsala Da Budurwar Sa


Matashin mai suna Kweku Mensah ya rataye kansa ne saboda sun yi hatsaniya da budurwar sa inda ta shaida masa cewa zata yanke alaka dashi marigayin. 

Al’amarin Ya faru ne a wani gari mai suna Axim dake arewacin kasar Ghana. Shugaban matasan yankin Axim Mista Kofi Nokoe ya shaidawa ma nema labarai cewa sun tsinci gawar mista kweku ne a rataye a jikin bishiya, inda daga nan suka rankaya da gawar zuwa asibitin yankin na Axim. 

You may also like