Man City da United sun kai zagayen kwata fayinal a Kofin Carabao



Earling Haaland

Asalin hoton, EPA

Makwabtan juna Manchester United da Manchester City sun kai zagayen kusa da na kusa da ƙarshe ko kuma kwata fayinal a kofin kalubale na Carabao.

City ta doke Liverpool a Etihad 3-2, ta hannun Erling Haaland da Riyad Mahrez da kuma Nathan Ake.

Ita kuma United ta doke Burnley ne 2-0.

A yanzu City za ta kara da Southampton wadda ta cinye Lincoln City, yayin da Man United za ta kara da Charlton Athletic.



Source link


Like it? Share with your friends!

0

You may also like