Manyan Hafsoshin Sojan Nijeriya Biyu Sunyi Ritaya



Shugaban Kasa, Muhammad Buhari ya amince da takardar yin ritaya da Shugaban Hafsoshin Nijeriya, Janar Gabriel Olonisakin da kuma Shugaban rundunar Sojan Ruwa, Vice admiral Ibok- Ete Ekwe Ibas suka mika masa.

Tuni dai Ministan Tsaro, Mansur Dan Ali ya nemi manyan hafsoshin kan su mika ragamar iko ga wadanda ke bin su a mukami wanda kuma ake sa ran Shugaban Rundunar Sojan Sama, Air Marshal Abubakar Sadik ne zai maye gurbin Shugaban hafsoshin Nijeriya a matsayin na riko kafin Shugaba Buhari ya yi sabon nadi.

You may also like